in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya halarci taron da ya shafi batun nukiliya na kasar Iran
2016-09-23 13:48:51 cri
A jiya Alhamis ne a hedkwatar MDD dake birnin New York na kasar Amurka kasashen nan 6 da batun nukiliya na kasar Iran ya shafa, wato Amurka,Birtaniya, Faransa, Rasha, Sin da Jamus, da kasar Iran din kanta suka shirya taron ministocin harkokin wajen kasashensu

A yayin taron, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin, mista Li Baodong, ya ce tun bayan da aka cimma yarjejeniyar daidaita batun nukiliyar kasar Iran a shekarar da ta gabata, zuwa yanzu ana aiwatar da yarjejeniyar yadda ya kamata. A cewarsa, kamata ya yi, kasashen 6 da bangaren Iran su kara yin mu'amala, don ganin an daidaita matsalolin da ake fuskanta a kokarin aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma.

Jami'in ya kara da cewa, kasar Sin tana goyon bayan yarjejeniyar, kuma tana kokarin kare ta. Saboda haka, nan gaba kasar Sin za ta ci gaba da musayar ra'ayi tare da bangarori masu ruwa da tsaki, tare da kokarin shiga aikin aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma kan batun nukiliyar kasar ta Iran.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China