in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ali Khamenei: Tsawaita wa'adin takunkumin da aka sakawa Iran ya sabawa yarjejeniyar makamashin nukiliya
2016-11-24 10:51:45 cri
Jagorin koli na kasar Iran Ali Khamenei, ya bayyana yayin da yake ganawa da wasu hafsoshi da membobin kungiyar sojojin fararen hula ta kasar ta Basij a jiya cewa, Amurka ta tsawaita wa'adin takunkumi da aka sakawa kasar Iran da shekaru 10, wanda ya sabawa yarjejeniyar makamashin nukiliya.

Khamenei ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Amurka ta yanzu ta gudanar da wasu ayyukan da suka sabawa yarjejeniyar makamashin nukiliya, ciki har da tsawaita wa'adin takunkumin da aka sakawa kasar Iran da shekaru 10. Idan aka aiwatar da kudurin, babu shakka wannan aiki ya sabawa yarjejeniyar makamashin nukiliya, kuma kasar Iran za ta mayar da martani.

A ranar 15 ga wannan wata, majalisar wakilan kasar Amurka ta amince da tsawaita wa'adin takunkumin da aka sakawa kasar Iran da shekaru 10 ta hanyar jefa kuri'u. A mahawarar da aka yi game da wannan batu, membobin majalisar wakilan Amurkar 419 ne suka jefa kuri'ar amincewa, daya ne tak ya ki amincewa. Yanzu haka an mika wannan kuduri ga majalisar dattijai ta kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China