in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta goyi bayan HKSAR wajen tabbatar da tsaro
2016-02-12 09:59:49 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya fada a daren Alhamis din da ta gabata cewar, gwamnatin tsakiya ta kasar Sin tana goyon bayan mahukunta yankin Hong Kong HKSAR da jami'an tsaron yankin wajen samar da tsaro da hukunta dukkanin bata gari bisa tanade tanaden dake kunshe cikin dokoki.

Hong Lei ya tabbatar da hakan ne a yayin da yake mayar da martani game da tarzomar da ta barke a yankin Mong Kok na Hong Kong tun a ranar Talatar da ta gabata.

Hong ya kara da cewa, wasu kungiyoyin 'yan ta da zaune tsaye ne masu neman ta ware suka kitsa ta da tarzomar a Mong Kok dake yankin Hong Kong tun a ranar 9 ga watan nan na Fabrairu.

Sanarwar ta kara da cewar, masu zanga zangar sun yi wa tituna a yankin kawanya inda suka cinna wuta, tare da lalata motocin jami'an 'yan sanda bayan sun jefi su da duwatsu, lamarin da ya haddasa jikkata jami'an 'yan sanda kimanin 89 da wasu 'yan jaridu.

Mista Hong ya kara da cewa, al'ummar yankin Hong Kong mutane ne masu kaunar zaman lafiya. Don haka gwamnatin tsakiya ta kasar Sin ta goyi bayan matakin da hukumar gudanarwar yankin da jami'an 'yan sandan suka dauka wajen tabbatar da tsaro a yankin, domin bada tsaro ga lafiya da dukiyoyin al'ummar mazauna yankin Hong Kong, sannan ta bukaci a zartar da hukunci kan duk wasu bata gari da aka samu da hannu wajen karya doka domin samun dawwaumammen zaman lafiya a Hong Kong. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China