in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sa ido ga jam'iyyar Kwaminis ta Sin yana da babbar ma'ana
2016-10-29 12:53:28 cri
An rufe cikakken zama na 6 na kwamitin tsakiya na karo na 18 na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin a ranar 27 ga wannan wata, inda aka mai da hankali game da matakin kara sa ido ga jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin a dukkan fannoni, da kuma yin bincike da zartas da ka'idojin harkokin siyasa na jam'iyyar a sabon mataki da ka'idojin sa ido ga jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin. Mutanen duniya suna maida hankali sosai ga wannan cikakken zama, a ganinsu, sa ido ga jam'iyyar Kwaminis ta Sin yana da babbar ma'ana.

Tsohon babban sakataren kwamitin kungiyar tarayyar turai EU, kuma Professor na kwalejin nahiyar Turai Gerhard Stahl, ya bayyana cewa, muhimman takardu da sanarwa da aka gabatar sun bayyana cewa, jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, tana kokarin dacewa da sauyin yanayi da ake ciki, da kasancewarta jam'iyya ta zamani, hakan ya shaida cewa, jam'iyyar tana da cikakkiyar niyyar yaki da cin hanci. Idan ana son raya tattalin arziki, tilas ne a yi yaki da cin hanci da gudanar da harkoki bisa dokoki.

Shugaban kwamitin harkokin duniya na Islamabad na kasar Pakistan Khaled Mahmoud, ya bayyana cewa, kara sa ido ga gudanar da harkokin jam'iyyar shi ne mihimmin mataki da JKS take aiwatarwa, ta haka ne za a kara gudanar da ayyukan gwamnatin kasar yadda ya kamata, da sa kaimi ga jama'a da su kara yin imani ga JKS. Kana wannan zai sa kaimi ga yin kwaskwarima a dukkan fannoni da kiyaye bunkasuwar tattalin arzikin kasar Sin, ta yadda za a amfanawa dukkan duniya baki daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China