in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira ga Amurka da Cuba su cigaba da raya huldar dake tsakaninsu
2016-10-27 10:56:31 cri

Wakilin kasar Sin a MDD Liu Jieyi, ya bayyana jiya Laraba cewa, kasar Sin tana fatan kasashen Amurka da Cuba za su cigaba da shimfida yunkurin raya huldar dake tsakaninsu yadda ya kamata, kuma Amurkar ta hanzarta dage takunkumin da ta kakabawa Cuba daga dukkan fannoni, wanda ya dace da cin moriyar bai daya ta kasashen dama jama'ar kasashen biyu. Wannan mataki zai taimaka wajen samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk nahiyar Amurka, tare da ci gaban al'ummar duniya baki daya.

A shekarar 1962 ne, shugaban Amurka na wancan lokaci John F. Kennedy, ya ba da umurni sanya wa Cuba takunkumi a fannonin tattalin arziki, da sha'anin kudi, da kuma cinikayya.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China