in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Argentina da Uruguay sun nuna sha'awar karbar bakuncin gasar FIFA ta 2030
2016-10-26 21:04:44 cri
Kasashen Argentina da Uruguay su nuna sha'awarsu ta karbar bakuncin gasar wasannin kwallon kafa ta duniya a shekarar 2030, wanda kuma shine zai tabbatar da cika shekaru 100 da fara wasannin kwallon kafa na FIFA.

Shugaban kasar Argentina Mauricio Macri da takwaransa na Uruguay Tabare Vazquez, suka sanar da hakan, bayan wata tattaunawar da shugabannin biyu suka gudanar a Buenos Aires.

A cewar Macri "za mu yi aiki tare, da nufin shiryawa tare da karbar bakuncin gasar wasannin kwallon kafa ta duniya a shekarar 2030.

Vazquez ya jaddada tasirin da zakarun yan wasan kwallon kafa na kasashen ke yi ga harkar wasannin kwallon kafa ta duniya.

Shugaban na Uruguay yace " ina magana ne kan Leo Messi da Luis Suarez,".

Wasannin na shekarar 2030, zasu tabbatar da cika karni guda da kasar ta Uruguay ta lashe kyautar gasar kwallon kafan ta duniya. Ana saran kwamitin shirya wasannin kwallon kafan ta duniya FIFA, zai yanke kuduri game da baiwa kasashen da zasu karbi bakuncin gasar wasannin kwallon kafan da za'a gudanar a shekarun 2026, da 2030 da kuma 2018.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China