in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara gina layin dogo da ya hada Nairobi da Malaba a kasar Kenya
2016-10-20 10:41:00 cri
A jiya Laraba ne aka kaddamar da aikin gina layin dogo da zai hada biranen Nairobi da Malaba na kasar Kenya, aikin da kamfanin kasar Sin China Communications Construction (CCC) zai gudanar da shi. Shugaban kasar Kenya, Uhuru Kenyatta, ya halarci bikin kaddamar da aiki, inda kuma ya sanar da bude aikin a hukunce.

An ce, bayan kammala layin dogon, zai hada layin Mombasa zuwa Nairobi da layin jirgin kasa dake cikin kasar Uganda, ta yadda za a samu damar rage kudin da ake kashewa wajen jigilar kayayyaki tsakanin sassan shiyyar dake gabashin Afirka. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China