Ministan tsaro gwamnatin yankin Galmudug dake tsakiyar kasar Somaliya ya bayyana a yayin taron manema labarai cewa, a wannan rana jirgin saman Amurka maras matuki ya kai harin kan kungiyar Al Shabaab, amma harin ya haddasa mutuwar sojojin Somaliya da dama. Wannan danyen aiki ya haddasa zanga-zanga a kasar. Kuma ya kara da cewa, watakila sojojin Amurka sun sami sakon asiri bisa kuskure. Don haka kamata ya yi Amurka ta yi bayani kan wannan harin da ta kai.
Rahotanni na cewa, Amurka ta jibge wasu sojojinta a Somaliya, da zummar ba da jagoranci da tallafawa wajen yaki da kungiyar Al Shabaab. A kullum sojojin Amurka su kan kan farmaki da jirgin sama maras matuki kan kungiyar Al Shabaab.(Fatima)