in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban FIFA ya bada shawarar kara yawan kungiyoyin da za su rika buga gasar cin kofin duniya
2016-10-05 14:00:29 cri
Shugaban hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA Gianni Infantino, wanda gabanin darewar sa kujerar jagorancin hukumar, ya alkawarta kara yawan kungiyoyin da zasu rika buga gasar cin kofin duniya wadda FIFA ke shiryawa, yanzu haka ya gabatar da wannan shawara ta kara yawan kungiyoyin zuwa 48.

Sai dai bisa shawarar da Infantino ya gabatar, kungiyoyi 16 daga wadanda za a kara zasu buga wasa daya daya ne na fidda gwanayen gasar, yayin da sauran kungiyoyin 32 za su ci gaba da buga gasar kamar yadda ake yi a baya.

Infantino, ya bayyana hakan ne yayin wani taro da ya gudana a jami'ar Arboleda, yana mai cewa za a yanke hukuncin karshe game da wannnan batu, yayin taron kwamitin zartaswar hukumar cikin watan Janairun shekara mai zuwa.

Ya ce burin hukumar FIFA shi ne ta gina harkar kwallon kafa a dukkanin fadin duniya, ta yadda za ta wuce batun gasa kadai, wato ta zamo harkar cudanya tsakanin al'ummar duniya.

An dai zabi Infantino a matsayin shugaban hukumar FIFA ne a ranar 26 ga watan Fabarairu, inda ya maye gurbin Sepp Blatter, wanda aka dakatar daga shiga harkokin wasanni na tsawo shekaru 6.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China