in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da bikin ba da lambar yabo ta sada zumunci ta gwamnatin Sin a Beijing
2016-09-30 10:57:08 cri
A yammacin jiya Alhamis 29 ga wata, an kaddamar da bikin ba da lambar yabo ta sada zumunci ta gwamnatin kasar Sin a Zhongnanhai dake birnin Beijing, inda memban hukumar siyasa ta kwamitin tsakiyar jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana mataimakin firaministan majalisar gudanarwa ta Sin, Ma Kai ya ba da lambobin ga masanan ketare tare da yin jawabinsa.

Ma Kai ya jaddada cewa, yanzu Sin tana gudanar da shirin raya kasa na shekaru 5 na 13, shi ya sa tana maraba da masana daga ketare da su samar da makoma mai kyau tare da jama'ar kasar Sin. Da fatan mafi yawan masanan ketare za su shiga aikin bunkasa kasar Sin, domin kara samar da sabbin kayayyaki a kasar. Bugu da kari, gwamnatin Sin za ta dauki kwararrun matakan shigar da gwanaye daga ketare, da gudanar da tsarin amincewa da mutanen kasashen waje wajen yin aiki a Sin, a kokarin ba da kariya ga iko da moriyar masanan ketare bisa dokoki, da samar da yanayi mai kyau ga ci gabansu.

Ana ba da lambar yabo ta sada zumunci ta gwamnatin kasar Sin ne domin yabawa masanan ketare da suka ba da babbar gudummawar zamanintar da kasar Sin. A bana, masana 50 daga kasashen waje 18 suka sami wadannan lambobi.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China