in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutunen da suka mutu a kwale-kwalen da ya kife a Masar ya karu zuwa 112
2016-09-23 20:28:28 cri
Rahotanni daga ma'aikatar lafiya ta kasar Masar na bayyana cewa, yawan mutane da suka mutu a wani hadarin kwale-kwale dauke da bakin haure da ya kife a kusa da arewacin gabar tekun Masar ya karu zuwa 112.

Kakakin ma'aikatar lafiya ta kasar Khaled Megahed ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua cewa, adadin yana iya karuwa,ganin cewa, har yanzu ana ci gaba da aikin ceto.

Bayanai na cewa, mahukuntan kasar Masar sun kama hudu daga cikin masu kwale-kwalen da ya kifen, bisa zargin su da laifin safarar mutane.

Hukumar kula da kan iyakokin kungiyar kasashen turai, ta yi gargadin cewa,yanzu haka ana kara samun bakin haure da ke kokarin shiga kasashen Turai ta tekun kasar Masar.

A ranar Larabar da ta gabata ce, wani kwale-kwale dauke da kimanin bakin haure 600 a kan hanyarta zuwa kasar Italiya ya kife a lardin Beheira da ke gabar tekun kasar Masar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China