Sanarwar hukumar ta bayyana cewa, yanzu haka 'yan wasan na Flamingoes suna samun horo a Abuja, babban birnin kasar. Kuma sun shirya tsaf don halartar wannan gasa da aka shirya gudanarwa daga ranar 30 ga watan Satumba zuwa 21 ga watan Oktoba.
A wani bangare na shirye-shiryen shiga wannan gasa, 'yan wasan na Flamingoes sun yi wasannin sada zumunci a gida.
Tawagar ta Najeriya tana rukuni na 3 ne wato C, inda za su kara da kasashe Brazil, Koriya ta Arewa da kuma Ingila. A ranar 26 ga watan Satumba ne ake sa ran 'yan wasan za su tashi zuwa kasar Jordan. (Ibrahim)