in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta kafa makarantun horas da matukan jiragen sama a Najeriya
2016-09-16 12:21:23 cri
MDD na bayyana aniyarta ta kafa wasu makarantun horas da matukan jiragen sama guda biyu a tarayyar Najeriya. Douglas Melvin shi ne shugaban shirin kafa makarantun, ya kuma bayyanawa manema labarai cewa, za a kafa makarantun ne a biranen Abuja da kuma Lagos, a wani mataki na baiwa kasar damar inganta harkokin sufuri, bisa managarcin tsari na tsaro da kariya ga masu amfani da jiragen sama.

Mr. Douglas ya ce an zabi Najeriya cikin kasashe 25, duba da irin kyakkyawar manufar kasar a fannin bunkasa harkokin sufurin sama. Kaza lika matakin zai ba da damar horas da ma'aikata sabbin dabarun wanzar da tsaro da kariya ga rayukan masu amfani da jirage. Har ila yau hakan zai samar da dama ta kwarewa a fannin dakile ayyukan 'yan ta'adda, wadanda sau da yawa kan yi kokarin amfani da kafar sufurin sama, wajen kaddamar da hare hare.

Game da hakan, ministan ma'aikatar sufurin saman kasar Hadi Sirika, ya ce Najeriya za ta samar da kananan kayayyakin bada horo da ake bukata a makarantun. Ya ce bayan kammalar aikin, makarantun za su zamo jigon cimma nasarar kudurin gwamnatin kasar, na kasancewar Najeriya daya daga manyan cibiyoyin zirga zirgar jiragen sama na shiyyar yammacin Afirka. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China