in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta lashi takwabin bunkasa bangaren tattalin arzikin da bai shafi mai ba
2016-09-02 11:23:11 cri
Gwamnatin Najeriya ta ce, ta dukufa ba dare ba rana don ganin ta farfado da bangaren tattalin arzikin kasar da bai shafi man fetur ba.

Ministar kudin kasar Kemi Adeosun ce ta bayyana hakan ga manema labarai a Abuja, fadar mulkin kasar, bayan kammala taron majalisar zartarwar kasar. Bayanan ministar dai na zuwa ne bayan da hukumar kididdigar kasar ta fitar da wasu alkaluma a ranar Laraba wadanda ke nuna cewa, tattalin azrikin Najeriyar ya yi kasa da kaso 2.06 cikin 100 a rubu'in na biyu na shekara.

Sai dai kuma ministar kudin ta karya zargin da wasu ke yi cewa, masu tsara manufofin tattalin arzikin kasar sun rude kuma ba za su iya ceto tattalin arzikin kasar ba.Ta kuma ce akwai alamar haske a tattalin arzikin kasar.

Shi ma shugaban majalisar 'yan kasuwa da masana'antu reshen Abuja, Tony Ejinkeoye ya ce, karayar tattalin arzikin da kasar ta ke fuskanta ya haifar da rashin aikin yi da wasu tarin matsaloli, kuma lamarin ka iya shafar bangaren ilimi,harkar zuba jari da sauran kananan sana'o'i.

A saboda haka, ya ce, akwai bukatar gwamnati ta gaggauta daukar kwararan matakan da suka dace don magance wannan matsala.

A nasa bangaren babban sakataren kungiyar kwadago ta Najeriya Peter Eson-Ozon, ya jaddada bukatar yiwa manufofin kasar gyaran fuska, ta yadda za a magance halin da tattalin arzikin kasar ya tsinci kansa a ciki.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China