in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan Najeriya sun yi fatali da kiraye-kirayen 'yan adawa na neman shugaba Buhari ya sauka daga mulki
2016-09-16 11:55:52 cri
Gwamnatin Najeriya ta sa kafa ta shure kiraye-kirayen da 'yan adawan ke yi na neman shugaba Muhammadu Buhari ya sauka daga karagar mulki.

A wata sanarwar da ministan watsa labarai da al'adu na kasar Lai Mohammed ya rabawa manema labarai, ministan ya soki kalaman jam'iyyar adawa ta PDP wadda ke kira ga shugaba Buhari da mukarrabansa da su sake dawo da tattalin arzikin kasar kamar yadda kowa ya san shi a baya kafin su hau karagar mulki a watan Mayun shekarar 2015.

Sanarwar ta ce, kalaman jam'iyyar adawar tamkar kora-kunya ne da hauka, da nufin dauke hankalin gwamnati daga kokarin da take yi na ceto kasar daga halin da ta shiga.

Ministan ya ce, gwamnati za ta ci gaba da karbar shawarwari masu ma'ana, domin ceto kasar daga halin da jam'iyyar ta PDP ta cusa kasar a ciki.

Lai Mohammed ya kara da cewa, gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari tana aiki ba dare ba rana domin farfado da tattalin arzikin kasar. Kuma za ta ci gaba da yaki da matsalar cin hanci da rashawa. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China