Mutane 38 sun rasa rayukansu sakamakon ambariyar ruwa a Nijar
Sabbin alkaluman da ofishin kula da harkokin jin kai na MDD dake Nijar ya fitar a jiya ya nuna cewa, ya zuwa yanzu kimanin mutane 38 ne suka mutu, yayin da 27 suka ji rauni, kana mutane kusan dubu 100 suka rasa gidajensu sakamakon bala'in ambariyar ruwa da ta shafi wasu sassan kasar a 'yan watannin da suka wuce. (Bilkisu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku