Manajan darektan bankin UBA a Najeriya Kennedy Uzoka ya ce an dauki wannan mataki ne, sakamakon karancin kudaden kasashen waje da 'yan Najeriyar suke bukata a kasuwa.
Uzoka ya ce, kafin a karawa 'yan canjin wadannan kudade da suke karba a bunkunan da aka ba su lasisin samar da kudaden, sai da babban bankin Najeriyar na CBN ya tattauna da kwamitin bankuna da wannan batu ya shafa, sakamakon rahotannin da ya samu na bukatar karawa 'yan canjin kudaden kasashen wajen.
Ya yi imanin cewa, wannan mataki zai taimaka wajen kara samarwa 'yan canjin isassun kudaden kasashe waje, daga bisani kuma ya rage farashin musayar dala a kasuwar canji.(Ibrahim)