A sanyin safiyar ranar 27 ga wata da misalin karfe 7 bisa agogon Libreville, hedkwatar kasar Gabon, an fara jefa kuri'ar zaben shugaban kasar, inda rumfunan zabe guda 2580 suka bude kofa ga masu jefa kuri'a kusan dubu 630.
Kwamitin zaben kasar ya ce, za a kammala kada kuri'a da karfe 6 na yamma a wannan rana, kuma za a gabatar da sakamakon zaben a ranar 30 ga wata. Bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulkin kasar Gabon, wanda ya fi samun yawan kuri'u shi ne zai zama sabon shugaban kasar. (Tasallah Yuan)