in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen BRICS su na kallon bunkasuwar kasashe a matsayin jigon ajandar samun dauwamammen ci gaba na shekarar 2030
2016-03-01 10:29:49 cri
A yayin taron karo na 31 na kwamitin kare hakkin dan Adam na M.D.D. wanda aka yi a ranar 29 ga watan Febrairu, wakilan kasashen BRICS wato Sin, Brazil, Rasha, India da na Afrika ta Kudu sun jaddada cewa, ya kamata a shigar da batun samun bunkasuwa cikin ajandar samun dauwamammen ci gaba ta shekarar 2030. Wannan shi ne karo na farko da kasashen BRICS suka gabatar da jawabi tare, a yayin taron kwamitin kare hakkin dan Adam na duniya.

A yammacin wannan rana, wakilan kasashen BRICS sun yi jawabi, inda suka bayyana cewa, batun samun bunkasuwa ya kasance tushen kawar da talauci, kuma talauci shi ne jigon barkewar rikice-rikice da dama a dukkanin fadin duniya. Kaza lika samun bunkasuwa na da tasiri ga kare hakkin dan Adam, yayin da kawar da talauci ya zama babban sharadi da burin samun dauwamammen ci gaba, da raya zamantakewar al'umma da kiyaye adalci, tare kuma da gina muhallin halittu.

Kasashen BRICS sun bayyana cewa, ya kamata a girmama manufofin kasashen duniya game da samun bunkasuwa, da kauracewa amfani da manufa guda, kasancewar kasashe da dama ne da mabambantan matakan bunkasuwa, da tarihi, da yanayin da kasashensu ke ciki, lamarin da ya sa ya kamata a sa kaimi ga kasashen duniya, wajen inganta dabarun raya kasashensu, da shirin samun dauwamammen ci gaba na shekarar 2030 na bai daya tare.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China