in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Najeriya ta gargadi 'yan kasarta da su guji zuwa kasashen Turai ba bisa ka'ida ba
2016-08-19 10:05:38 cri
A jiya ne mahukuntan Najeriya suka gargadin 'yan kasarta da su guji shiga kasashen Turai ta barauniyar hanya.

Ministan kwadago da samar da aikin yi na Najeriya Chris Bgige ne ya yi wannan gargadi a Abuja, babban birnin kasar, a lokacin bikin kaddamar da manufofin kasar game da kaurar ma'aikata wanda kungiyar kula da kaurar jama'a ta kasa da kasa(IOM) da kungiyar kwadago da duniya(ILO) suka tsara.

Minista Ngige, ya bayyana cewa, wasu jaridun cikin gida da na kasashen duniya sun wallafa wasu rahotanni game da 'yan Najeriyar da suka rasa rayukansu a kokarin shiga kasashen Turai ta tekun Bahar Rum da Hamadar Sahara.

Ya ce, gwamnatin Najeriya tana dora muhimmanci sosai kan dokokin da suka shafi kwadago, kasancewarta kasa mai asali da kyakkyawar makoma, haka kuma tana amfana da gudummawar da ma'aikatan suke bayarwa.

Ngige ya ce, an inganta wannan doka ce, saboda hadarin da ke tattare da kaurar da jama'a suke yi ba bisa ka'ida ba da kuma tasirin hakan ga albarkatun kasa da kuma ci gabanta.

Tun da farko a nasa jawabin, babban jami'in kungiyar kula da kaurar jama'a ta kasa da kasa(IOM) ya ce, akwai bukatar daukar muhimman matakan aiwatar da wadannan manufofi, ta yadda haka za ta cimma ruwa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China