Shugaba Xi ya ba da umarnin a kara tura sojoji wuraren da bala'in ambaliya ruwa ta shafa
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya umarci rundunonin soja da na 'yan sandan kasar da su kara tura dakaru don ba da taimako wajen dakatar da almbaliyar ruwa da gudanar da aikin jin kai a yankunan da ruwan sama kamar da bakin kwarya ya yi wa barna.
Ma'aikatar kula da harkokin jama'a ta kasar Sin ta bayyana a jiya Talata cewa, mutane 128 ne suka mutu kana wasu 42 suka bace, sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shafe kwanaki biyar ana yi a yankin kogin Yangtze da wuraren da ya ratsa.(Ibrahim)