Ban ya bayyana goyan baya da kuma yawaba kokarin AMISOM da dakarun sojin kasar Somali wajen kwarewarsu da kuma jarumtar da suke nunawa wajen murkushe masu kaddamar da hare hare a kokarinsu na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar Somaliya.
Kungiyar Al-Shabaab ta dauki alhakin kaddamar da harin, kuma tace ta hallaka a kalla sojojin kasar Habasha 60 a sansanin sojin.
Sai dai AMISOM ta musanta ikirarin da Al-Shabaab tayi, tana mai cewa dakarunta sun samu nasarar fatattakar maharan.