in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Afrika na fatar taron G20 zai tabo batun masana'antun Afrika
2016-07-17 12:16:32 cri
Shugaban kasar Senegal Macky Sall ya fada cewar, shugabannin Afrika na sa tsammanin taron kasashe 20 mafiya karfin tattalin arziki a duniya na bana wanda kasar Sin zata jagoranta zai tabo batun sabbin hanyoyin bunkasa cigaban masana'antu a nahiyar Afrika.

Sall yace, Afrika tana maraba da matakan da zasu taimaka wajen habaka cigaban masana'antu a nahiyar, kuma tana fatar taron da za'a gudanar a watan Satumba na kasashen 20 mafiya karfin tattalin arziki a duniya zai waiwayi wannan muhimmin batu.

Shugaban na Senegal ya fada a yayin taron kwamitin shugabanni Afrika karo 27 na taron hadin gwiwar cigaban kasashen Afrika NEPAD karo na 35 a Kigali babban birnin Rwanda cewar, samar da manufofi na hadin gwiwa a tsakanin kasashen nahiyar, zai habaka cigaban masana'antu da inganta rayuwar al'umma mazauna nahiyar.

Yace jagorancin da kasar Sin zata yi ga taron, wata babbar dama ce ta kara hadin gwiwa tsakanin nahiyar Asiya da Afrika wajen bunkasa cigaban ababan more rayuwa.

Ana saran kudurorin da za'a cimma za su bada dama wajen habaka cigaban kimiyya da fasaha, da kirkire kirkire da kananan sana'oi.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China