in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sinawa fiye da 70 aka kwashe daga hedkwatar kasar Sudan ta kudu zuwa kasar Kenya
2016-07-13 11:42:18 cri

A jiya Talata da dare, Sinawa fiye da 70 sun tashi daga birnin Juba, hedkwatar kasar Sudan ta Kudu, inda ake fama da tashe-tashen hankali zuwa birnin Nairobi na kasar Kenya.

An ba da labari cewa, galibin Sinawa da suka isa birnin Nairobi su ne ma'aikatan kamfannonin Sin dake kasar Sudan ta kudu.

Ma ba da taimako ga babban wakilin kamfanin samar da wutar lantarki na kasar Sin dake kasar Sudan ta kudu Wang Cun ya bayyana cewa, a jiya Talata, kura ta lafa a birnin Juba, lamarin da ya baiwa mutanen kasashen waje da dama barin kasar Sudan ta kudu.

Mr. Wang ya ce, bayan barkewar rikicin, ofishin jakadanci na kasar Sin dake kasar Sudan ta kudu ya tuntubi kungiyar kasuwanci ta Sin da kamfannoni kasar Sin dake kasar, domin gabatar da shawara da kuma taimakawa ma'aikata Sinawa wajen tashi daga birnin Juba. Bisa taimakon da aka bayar, ofishin jakadancin Sin ya tabbatar da wurare 9 inda Sinawa za su taru don kwashe daga birnin Juba.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China