in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin ta'addanci a Iraki
2016-07-04 11:19:34 cri
A jiya Lahadi, babban sakataren MDD Ban Ki-moon da shugaban babban taron MDD Lykketoft sun ba da sanarwar yin Allah wadai da harin ta'addanci da aka kai a wannan rana a birnin Bagadaza, hedkwatar Iraki, inda suka yi kira ga gwamnatin Iraki da ta gaggauta gurfanar da masu aikata laifin a gaban kotu.

A cikin sanarwar, Ban Ki-moon ya bayyana cewa, a yayin da mazauna wurin suke share fagen maraba da bikin karamar sallah, maharan sun kaddamar da harin ta'addanci, wannan ya girgiza shi sosai.

Ban Ki-moon ya yi kira ga jama'ar Iraki da su yaki kowane irin yunkurin jefa tsoro da wargaza hadin kansu, sannan ya yi kira ga gwamnatin kasar da ta cafke wadanda suka aikata laifin tun da wuri.

A nasa bangare, mista Lykketoft ya bayyana a sanarwar cewa, wannan harin ta'addanci ya haddasa mutuwar fararen hula da yawa, ciki har da yara kanana da dama, kamata ya yi a yi suka kan wannan hari da babbar murya. Ya ce, MDD za ta hada kanta da jama'a da gwamnatin Iraki domin yaki da ta'addanci.

A jiya wani jami'in Iraki ya furta cewa, a safiyar wannan rana, an kai harin tagwayen boma-bomai da aka dasa cikin mota a birnin Bagadaza, wadanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 126, yayin da wasu 147 suka jikkata. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China