in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban bankin kasar Sin ya zargi wasu kafofin watsa labaru da bayar da labaru domin yunkurin rage darajar kudin RMB
2016-07-01 10:39:48 cri
A jiya, 30 ga watan Yuni, bankin jama'ar kasar Sin, wato babban bankin kasar ya fitar da wata sanarwa, inda ya ce, a kwanan baya, wasu kafofin watsa labaru sun yi ta bayar da labarun da ba su da tushe game da sauyin darajar kudin RMB domin yunkurin kawo matsala ga aikin tafiyar da kasuwar cinikin kudaden kasashen duniya a wannan lokaci dake janyo hankalin jama'a sosai. A hakika dai, sun taimakawa wasu 'yan kasuwa da su rage darajar kudin RMB. Tun da haka, babban bankin kasar Sin ya zargi irin wadannan matakan da suke sabawa ka'idojin aikin jarida ba kamar yadda ya kamata ba.

A cikin sanarwar, babban bankin kasar Sin ya bayyana cewa, a 'yan kwanaki, kasuwannin cinikin kudaden duniya sun samu sauye-sauye sosai sakamakon ballewar Burtaniya daga kungiyar tarayyar Turai EU. Lamarin ya kuma sa darajar kudin RMB ta samu dan raguwa. Amma yanzu ana cinikin kudin RMB a kasuwa bisa dokokin da aka tsara kamar yadda ya kamata. Darajar kudin RMB ba ta samu sauye-sauye sosai ba.

Sannan, wannan sanarwa ta ce, an yi hasashen cewa, tattalin arzikin kasar Sin zai ci gaba da samun bunkasa cikin sauri, kuma yana da karfin yin takara a duniya gaba daya. Bugu da kari, kasar Sin tana da isassun kudaden waje da ta ajiya da kasafin kudi. Kasar Sin ba ta da shirin rage darajar kudin RMB domin kara karfin takara domin fitar da kayayyakinta zuwa kasashen duniya. Halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki ya alamanta cewa, babu wani dalilin rage darajar kudin RMB da zai kasance cikin dogon lokaci a nan gaba ba. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China