in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Rasha ta tsawaita wa'adin takunkumin da ta saka wa kasashen yammacin duniya
2016-06-30 13:36:30 cri
A jiya ne shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin, ya sa hannu kan wani umarnin da ya bayar, inda ya tsawaita wa'adin takunkumin da kasar ta kakabawa kasashen yammacin duniya, daga ranar 6 ga watan Augustan shekarar 2016, karshen wa'adin da aka tanada a baya, zuwa karshen shekarar 2017.

Bayan barkewar rikici a kasar Ukraine ne, kasar Amurka da kasashen kungiyar tarayyar Turai EU suka fara sanyawa kasar Rasha takunkumi, abin da ya sanya shi ma shugaba Putin na kasar Rasha ya ba da umarnin hana shigowa da kayayyakin amfani gona, da abinci daga kasashen da suka kakabawa kasarsa takunkumi.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China