in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kashe sojoji 15 da 'yan tawaye a gabashin RD-Congo
2016-06-28 11:29:32 cri
Kakakin ayyukan Sokola 2, mista Mac Azukayi ya bayar da wata sanarwa a birnin Goma na gabashin kasar jamhuriyyar demokaradiyar Congo , cewar, rundunar sojojin kasar (FARDC) ta bayyana cewa sojoji 15 ne suka mutu daga bangarenta yayin da 37 suka mutu daga bangaren 'yan tawayen Uganda na ADF a yayin wasu ayyukan samame da aka fara tun cikin watan da ya gabata kan 'yan tawayen ADF a gabashin kasar. An cafke wasu 'yan tawaye 15, da sanya hannu kan makamai da harsasai, wadanda suka hada da bindigogi kirar AK-47 guda 13, da boma bomai kirar hannu.

Rundunar Congo ta samu goyon bayan dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD dake kasar (MONUSCO), kana kuma ayyukan da aka kaddamar tun cikin watan da ya gabata kan mayakan ADF, sun yi sanadiyyar mutuwar mutane dubbai a yankin Beni dake arewacin Kivu.

A gundumar Ituri, mayakan sa kai na kungiyar 'yan tawayen Ituri (FRPI) guda 10 aka kashe a yayin wani gumurzu tsakanin rundunar sojojin FARDC da mayakan a kauyen Kienge na masarautar Walendu Bindi a ranar Litinin da ta gabata.

A cewar majiyoyin soja, gumurzun ya barke a lokacin da sojojin FARDC suka fara ayyukan zakulo sansanonin mayakan sa kai dake kokarin sake hadewa tun fiye da mako guda da ya gabata a wannan yanki na gundumar Ituri.

A cikin wata sanarwa, komandan na biyu na bangaren FARDC dake Ituri ya bayyana cewa wadannan 'yan tawaye na yunkurin sake hadewa domin yawaita hare-harensu kan fararen hula. (Maman Ada) 

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China