in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a ci gaba da kokarin dunkulewar kasa da kasa a fannin raya tattalin arziki, in ji Barack Obama
2016-06-25 13:22:55 cri
Jiya Jumma'a 24 ga wata, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya bayyana a yayin bikin rufe taron kolin kafa kamfanoni na kasa da kasa cewa, za a ci gaba da kokarin dunkulewar kasashen duniya ta fuskar raya tattalin arziki a nan gaba, ya kuma yi kira ga gwamnatoci da kamfanonin kasa da kasa da su samar da taimako ga wadanda suke son kafa kamfanoni.

Haka zalika ya ce, ficewar Burtaniya daga kungiyar tarayyar kasashen Turai ta kasance wani babban kalubale ga dunkulewar kasa da kasa baki daya, amma, yana imanin cewa, tabbas ne kasashen duniya za su ci gaba da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a nan gaba, kuma wadannan mahalarta taron dake son kafa kamfanonin kansu za su samar da dama mai kyau wajen raya hadin gwiwar kasa da kasa.

Bugu da kari, Mr. Obama ya ce, tun da aka bullo da taron kafa kamfanonin kasa da kasa a shekarar 2009, ya tattauna da masu kafa kamfanoni da dama, ya gane wahalar da suka sha sosai a wannan fanni, shi ya sa, yana fatan gwamnatoci da kamfanonin kasa da kasa, har ma da gamayyar kasa da kasa baki daya za su iya samar wa matasa wandanda suke son kafa kamfanoni taimako yadda ya kamata, ta yadda za a iya kyautata yanayin tattalin arzikin duniya cikin hadin gwiwa.

Masu kamfanoni, masu zuba jari da kuma matasa masu son kafa kamfanoni sama da dubu daya da suka zo daga kasashe kimanin 170 sun halarci taron da aka yi a Silicon Valley na kasar Amurka, kuma taron na shekara mai zuwa, za a yi shi a kasar India. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China