Kasar Sin ta yaba wa Rasha kan yadda ta bayyana ra'ayinta game da batun tekun kudancin Sin
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yau Alhamis a nan birnin Beijing cewa, ra'ayin da kasar Rasha ta bayyana game da batun tekun kudancin Sin ya bayyana hakikanin yanayin da yankin ke ciki, yana kuma wakiltar muryar adalci ta duniya kan batun. Saboda haka, kasar Sin ta nuna yabo sosai da hakan.
Kwanan bayan jakadan kasar Rasha dake kasar Sin ya bayyana cewa, al'amura sun tsananta a yankin tekun kudancin Sin sakamakon tsoma bakin da wasu kasashen da ba na shiyyar ba suka yi. (Bilkisu)