in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da bikin "Sa ido kan al'adun kasashen Afirka" a birnin Beijing
2016-05-09 10:28:26 cri
A kwanan baya, an kaddamar da babban biki mai taken "Sa ido kan al'adun kasashen Afirka na shekarar 2016" kana bikin nune-nune na "Alamar kasashen Afirka" a dakin adana kayayyakin tarihi na mata da yara dake birnin Beijing, inda mahalarta bikin daga Sin da ketare sama da 300 suka halarci wadannan ayyuka.

Bikin "Sa ido kan al'adun kasashen Afirka na shekarar 2016", wani muhimmin kashi ne na fannin al'adu dake cikin shirin ayyukan Johannesburg daga shekarar 2016 zuwa ta 2018 na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka. Bana ma'aikatar al'adu ta Sin za ta gayyaci kungiyoyin nuna fasahohi daga kasashen Afirka sama da 20 zuwa kasar Sin, domin nuna fasahohi da yin bikin nune nune sama da dari daya a larduna da birane sama da 10 na Sin. A matsayin wani muhimmin mataki na bikin "Sa ido kan al'adun kasashen Afirka na shekarar 2016", an kaddamar da bikin nune-nunen zane-zane mai taken "Alamar kasashen Afirka" a sa'i daya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China