A jiya Litinin a birnin Dakar, fadar mulkin kasar Senegal, an bude rumfar kasar Sin a wurin bikin nune-nunen wasannin fasaha na shekaru biyu-biyu da kasar ke shiryawa. Wannan karo shi ne na farko da kasar ta Sin ta shiga wannan bikin nune-nune da ake yi a kasashen dake kudu da hamadar Sahara.(Lami)