Mr. Hoc, wanda ya zanta da wakilin kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, ya ce nan gaba kadan, yaran da tashe tashen hankula na kabilanci suka raba da makarantu, za su samun damar komawa azuzuwa domin fara darussa.
Ya ce muhimmin aikin da za su sanya gaba shi ne kara gina makarantu, da daukar sabbi, tare da horas da malaman makaranta, kasancewar yanzu haka bisa kiyasi, malami guda na kula da yara da yawan su ya kai 150.
A baya ma wakilin asusun yara na UNICEF a Sudan ta Kudun Jonathan Veitch, ya taba bayyana cewa Sudan ta kudun ce ke kan gaba a duk duniya, wajen yawan yara kanana da ba sa zuwa makaranta sakamakon yakin basasa da ya daidaita kasar.
A cewar sa akwai yara sama da miliyan daya da dubu dari 8, wato sama da rabin yaran kasar, wadanda ba su da damar zuwa makaranta. (Saminu)