in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya gana da takwararsa ta Jamus
2016-06-13 11:12:11 cri
Firaministan majalisar gudanarwa ta kasar Sin Li Keqiang ya gana da takwararsa shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel, wadda ke yin ziyarar aiki a nan birnin Beijing na kasar Sin da kuma halartar taron musayar ra'ayi a tsakanin gwamnatocin kasashen biyu karo na 4.

Mr. Li ya bayyana cewa, kasar Sin ta yi amana ga hulda da hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Jamus. Kasar Sin tana maraba da kamfanonin kasar Jamus da na sauran kasashen duniya wajen zuba jari a kasarta. Sannan yana fatan kasashen Sin da Jamus za su karfafa hadin gwiwarsu da kara yin musayar ra'ayi a kungiyar G20, da kuma dukufa kan bunkasuwar tattalin arzikin duniya tare, domin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

A nata bangaren, Angela Merkel ta bayyana cewa, huldar dake tsakanin kasashen Jamus da Sin tana samun bunkasuwa sosai. A matsayin wani muhimmin tsari, taron musayar ra'ayi a tsakanin gwamnatocin kasashen biyu ya ingiza bunkasuwar hadin gwiwa a tsakanin bangarorin biyu a dukkan fannoni. Kasar Jamus tana son tabbatar da "shirin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Jamus" da kasashen biyu suka tsara a gun taron musayar ra'ayi a tsakaninsu karo na 3 tare da kasar Sin, da kuma kiran taron musayar ra'ayi karo na 4 yadda ya kamata, domin inganta hulda da hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China