in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar zaben Ghana za ta yi rijistar sabbin masu kada kuri'a kimanin miliyan 1.2
2016-04-29 09:52:30 cri
Tun a ranar Alhamis data gabata ne, hukumar zaben kasar Ghana ta fara yin rijistar sabbin masu kada kuri'a da adadinsu ya kai miliyan 1 da dubu 200 a yayin da ake tunkarar babban zaben kasar a karshen wannan shekara.

A yanzu haka an bude cibiyoyin yin rijista kimanin 3,500 domin yin rijistar har na tsawon kwanaki 10 ga al'ummar Ghana 'yan shekaru 18 zuwa sama, domin su samu damar kada kuri'unsu a babban zaben kasar dake tafe.

Sai dai hukumar zaben kasar ta gargadi jama'a da su guji yin rjistar fiye da sau daya, kasancewar na'ura zata iya gano masu wannan yunkuri.

Za'a kammala aikin rijistar ne a ranar 8 ga watan Mayu, kuma za'a gudanar da babban zaben kasar a watan Nuwambar bana.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China