in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cote d'Ivoire da Guinee na fatan karfafa dangantakarsu ta fuskar soja domin dakile ta'addanci
2016-05-31 13:15:52 cri
Ministocin tsaron Cote d'Ivoire da Guinee sun bayyana a ranar Litinin niyyar kasashen biyu na karfafa dangantarkarsu ta fuskar soja da zummar dakile ta'addanci yadda ya kamata.

Ministan tsaron Cote d'Ivoire Alain Donwahi, a yayin ganawar aiki ya ce, mu kasashe ne 'yan uwan juna dake makwabtaka. Muna raba damuwa guda ta fuskar tsaro kuma yana da fa'ida mu gamu domin yaki da dukkan bala'un dake kawo illa ga yanayin tsaron mu.

A cewarsa mista Donwahi, bukatar tsaron hadin gwiwa da musanyar kwarewa tsakanin kasashen biyu nada muhimmancin gaske.

A nasa bangare, ministan kasa na Guinee dake fadar shugaban kasa mai kula da harkokin tsaro Mohamed Diane ya nuna cewa an samu sakamako mai alfamu da makoma mai haske game da musanyar kwarewa a fannin gyare gyaren rundunar sojojin kasashen biyu.

A cewarsa, hadin gwiwar ayyuka zai taimaka wajen jajircewa yadda ya kamata game da dabarun da za amfani da su wajen yaki da ta'addanci, domin tabbatar da zama lafiya da kulawa mai kyau kan iyaka tsakanin Cote d'Ivoire da Guinee. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China