in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso na shirin janye rabin sojojinta daga yankin Darfour
2016-05-15 17:22:50 cri

Domin kalubalantar barazanar ta'addanci a doron kasarta, Burkina Faso, kasa ta goma sha daya dake taimakawa MDD dake sojoji, na shirin janye rabin sojojinta dake yankin Darfour, a cewar ma'aikatar tsaron kasar.

Tare da bullowar kungiyoyin ta'addanci a kasar Mali, idan da gamayyar kasa da kasa ba ta tura sojoji ba domin kawo dauki ga shiyyar, da akwai yiyuwar cewa kungiyoyin ta'addanci dake dauke da makamai ba zasu tsaya a arewacin tafikin Nijar ba amma zasu wuce nan, in ji manjo janar na rundunar sojojin Burkina Faso, Pingrenoma Zagre.

Kasar Burkina Faso, kamar sauran kasashen shiyyar yammacin Afrika na fama da barazanar ta'addanci.

A tsakiyar watan Janairu, wani harin ta'addanci da kungiyar Al-Qaida reshen yankin Maghreb wato AQMI yayi sanadiyyar mutuwar mutane kusan 30. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China