in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso: Jam'iyyu 26 sun kafa wani kawance domin goyon bayan shirin shugaba Kabore
2016-04-08 10:33:46 cri
Jam'iyyun siyasa 26 ne suka kafa a ranar Alhamis a birnin Ouagadougou, wani kawancen jam'iyyu da kungiyoyin siyasa na masu rinjaye (APMP) domin kawo goyon baya ga shirin shekaru biyar na shugaban kasar, Roch Marc Christian Kabore da ya yi bitar kwanakin dari a kan mulki.

Jam'iyyun APMP suna goyon baya da ba da kwarin gwiwa ga gwamnatin kasar da ta cigaba da kawo sauye sauyen tattalin arziki, jama'a da siyasa domin cigaban kasar, in ji kakakin wannan kawance, Adama Kanazoe, wanda shi ma ya kasance shugaban kawancen matasa domin 'yanci da jamhuriyya (AJIR), a yayin wani taron manema labarai. Ya kuma jaddada cewa APMP, wani gungun jam'iyyu da kungiyoyin siyasa ne dake goyon baya da kuma kare shirin siyasa na shugaba Kabore da kuma cigaban aiwatar da shi. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China