in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a sanya batun samu ci gaba a sahun farko a ajandar taron kolin G20
2016-05-26 19:22:43 cri
A yau Alhamis ne ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya ce, taimakawa kasashe masu tasowa wajen kawar da talauci, da tabbatar da samun dauwamammen ci gaba nauyi ne da ya rataya a wuyan kasashen duniya baki daya, kana zai taimaka ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya.

Wang Yi ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labaru da ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta shirya a wannan rana game da taron kolin G20 na Hangzhou.

Wang ya kara da cewa, kasar Sin kasa ce mai tasowa mafi girma a duniya, saboda haka ta fahimci muhimmancin bunkasuwa sosai. An zabi kasar Sin domin shirya taron kolin G20, don haka ya dace a sanya batun bunkasuwa a muhimmin matsayi, kuma wannan fatan ne na kasashe masu tasowa baki daya, kana nauyi ne da ya kamata kasar Sin ta dauka. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China