in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An shirya taron kolin G20 da za a yi a birnin Hangzhou cikin armashi
2016-05-26 11:03:32 cri
A ranar 4 da ta 5 ga watan Satumbar bana, za a yi taron kolin kungiyar G20 a birnin Hangzhou dake kasar Sin. Ranar 27 ga watan nan, saura kwanaki 100 cif a bude taron, kuma an riga an fara gudanar da ayyukan share fagen gudanar taron yadda ya kamata.

Yanzu haka dai an kammala aikin kyautata gine-ginen wuraren karbar taron kolin, da wuraren da shugabannin za su zauna, da ragowar sauran wurare, ana kuma shiga matakan karshe na kyautata yanayi a wurin.

Sakataren gwamnatin birnin Hangzhou Zhao Yide, ya ce yana fatan amfani da wannan taro, don sanarwa duniya yanayin da kasar Sin ke ciki, da nasarorin da Sin ta samu ta hanyar gudanar da manufar gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje, kana da zamanintar da kasar, da halayyen Sinawa.

Ya zuwa yanzu, an kusan kammala dukkanin ayyukan sharen fagen, nan gaba kuma za a ci gaba da ba da tabbaci don gudanar da wasu hidimomi, don tabbatar da gudanar taron cikin nasara.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China