in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin man fetur na Eni ya ambato matsalar da ta fi karfinsa bayan wani harin bututunsa a Najeriya
2016-05-26 10:52:46 cri
Kamfanin hakar man fetur na Eni ya sanar a ranar Talata cewa ya bayyana wani halin da ya fi karfinsa a Najeriya bayan wani hari kan bututunsa na fitar da man fetur dake yankin Bayelsa na Niger Delta, ranar Lahadin da ta gabata.

A cikin wata sanarwa, kamfanin, dake aiki tare da kamfanin man fetur na Agip na Najeriya (NAOC), ya bayyana cewa harin na ranar Lahadi kan bututunsa dake jihar Bayelsa ya rage samar da man fetur dinsa na gangunan mai 4200 a kowace rana.

Wannan na sa kamfanonin sun kasa cika alkawuransu na aiki dalilin abubuwan da suka wuce ikonsu.

A farkon watan Mayu, Kamfanonin Shell da Exxon Mobil sun bayyana matsalar da ta fi karfinsu a yankin Niger Delta, inda masu fafatuka suka fara kai hare-hare da janyo wani ja da baya ga fitar da man fetur daga Najeriya.

A ranar Laraban da ta gabata, wani harin ya janyo asarar kimanin gangunan mai 1000, tare da haddasa wata asarar ajimilce ta samar da gangunan mai 5200 a bangaren kamfanin hakar mai na Eni.

A ranar, gwamnatin Najeriya ta sanar da daura damarar yaki da kungiyar Niger Delta Avengers (NDA), wani sabon gungun masu fafutuka dake yankin, domin kawo karshen hare hare kan gine ginen man fetur da gas. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China