Ministan wanda ya bayyana hakan, yayin taron zantawa da jam'iyyun gama kai da ya gudana jiya Litinin a jihar Legas, ya ce matakin janye yajin aikin na da matukar fa'ida ga 'yan kasar.
Daga nan sai ya jaddada aniyar gwamnatin kasar mai ci, na cika alkawuran da ta daukarwa 'yan kasar, yayin da a hannu guda kuma, za ta rika tattaunawa da 'yan kasar da nufin jin ta bakin su game da hakan. (Saminu Hassan)