in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: za a dauki kwararan matakai kan tsagerun Niger Delta
2016-05-24 09:41:34 cri
Babban hafsan rundunar tsaron Najeriya Janar Abayomi Olonishakin, ya ce rundunar sojin kasar na ci gaba da nazartar halin da ake ciki a yankin Niger Delta mai arzikin man fetur, da nufin daukar matakan da suka kamata, na kawo karshen fasa bututan mai da tsagerun yankin ke aikatawa.

Janar Olonishakin ya ce ko shakka babu, rundunar za ta fuskanci kalubalen da tsagerun kungiyar Niger Delta Avengers ke haifarwa a yankin, ko da yake a cewar sa ba ya ga dabarun yaki, rundunar za kuma ta tattauna da masu ruwa da tsaki a yankin, da nufin lalubo hanyoyin ba da kariya ga bututan mai da na iskar gas, wadanda ke matukar fuskantar barazana daga tsagerun yankin. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China