in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Takaitattun labarai daga jaridun Najeriya
2016-05-24 19:16:05 cri
Hukumar nan da ke sanya don ganin an tabbatar da gaskiya a bangaren ma'adinai ta Najeriya(NEITI) ta zargi kamfanin man fetur na kasar wato NNPC da sauran kamfanonin mai da iskar gas da kin saka dala biliyan 4.4 da kuma Naira biliyan 358.3 wato kimanin dala miliyan 1.79 a cikin asusun ajiyar gwamnatin tarayya.(Vanguard)

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya karyata rahotanni da wasu jaridun kasar ke yayatawa a jiya cewa, yana shirin neman mafakar siyasa a daya daga cikin kasashen da ke yammacin Afirka, sakamakon rahoton da ke cewa, hukumar EFCC mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasar zagon kasa tana shirin bincikar gwamnatinsa da ta gabata bisa zargin aikata cin hanci da rashawa.

Sai dai kakakinsa Reno Omokri, ya ce tsohon shugaban kasar ya ba shi tabbacin cewa, zai dawo Najeriya da zarar ya kammala ziyararsa a birane daban daban.(The Guardian)

Mai magana da yawun rundunar sojojin Najeriya kanar Sani Usman ya ce, daya daga cikin manyan masu harhadawa kungiyar Boko Haram bama-bamai ya gamu da ajalinsa, sakamakon yadda wani dan kungiyar ya harbe shi a lokacin da yake kokarin tserewa daga cikin kungiyar a jiya Litinin.

Kanar Sani ya bayyana lamarin a matsayin wani muhimmin ci gaba a yakin da dakarun kasar ta Najeriya suke yi na kakkabe 'yan ta'addan.(Daliy Trust)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China