A jiya Lahadi ne babbar kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC) ta dakatar da yajin aikin da yi niyyar shiga a duk fadin kasar a ranar Larabar da ta gabata, domin nuna adawa da karin farashin kudin mai da gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi. Wata sanarwar da gwamnatin Najeriya ta fitar a daren jiya,ta yi maraba da shawarar kungiyar kwadagon na dakatar da shiga yajin aikin, inda ta bayyana kudurinta na hawa teburin sulhu da 'yayan kungiyar.(Daily Trust)
Rundunar 'yan sandan Najeriya ta girke jami'anta a hedkwatar jam'iyyar PDP da ke Abuja,fadar mulkin kasar. Rundunar 'yan sandan ta dauki wannan mataki ne a jiya,don hana barkewar duk wani tashin hankali a sakatariyar jam'iyyar.( The Punch)