in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kara yawan majalisar ministoci a Jamhuriyar Nijar
2016-05-19 10:16:18 cri
Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa, yanzu haka yawan majalisar ministocin kasar ya karu zuwa 41, tun bayan da shugaban kasar ya sanar da sabuwar majalisar ministocinsa mai kunshe da wakilai 38, bayan da aka sake zabensa a ranar 20 ga watan Maris din wannan shekara.

A ranar Talata ce shugaban kasar Mahamadou Issoufou ya sanya hannu kan wata sabuwar doka, inda ya nada Ahmat Jidoud a matsayin ministan kasafin kudi.

Shugaba Issoufou ya kuma nada wani tsohon jagoran 'yan tawaye Rissa Ag Boula a matsayin minista a ofishin shugaban kasa, yayin da ya nada Chika Rakiato Bako mukamin minista mai kula da raya yankunan karkaka.

Brigi Rafini ne ke rike da mukamin firaministan gwamnatin Nijar din mai ministoci 41, 7 daga cikinsu kuma mata ne. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China