in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban bankin Najeriya na gudanar da bincike kan wasu bankunan kasar
2016-05-10 10:34:51 cri
Kakakin babban bankin Najeriya CBN Mr. Issac Okorafor, ya ce bankin na gudanar da hadin gwiwa da wasu hukumomin bincike, game da hada-hadar kudade da wasu bankunan kasar suka gudanar, wadanda mai yiwuwa ne sun sabawa doka.

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun Mr. Okorafor, ta ce bankin na CBN na binciken ne domin gano hakikakin gaskiyar wasu zarge zarge da ake yiwa wasu daga bankuna cinikayyar kasar. A cewar sa za a ci gaba da aiwatar da hakan a kai a kai, musamman ma kan hada hada da ta shafi bankunan dake da alamar tambaya.

Sanarwar ta kara da cewa kare martabar tsarin da Najeriya ke bi wajen gudanar da harkokin kudi na da matukar muhimmanci, don haka ya zama wajibi bankuna da masu hulda da su, su kaucewa amfani da bankunan wajen aiwatar da huldodi da suka sabawa doka.

Yanzu haka dai hukumar EFCC mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin Najeriyar kafar ungulu, na binciken wasu manyan manajojin bankin Fidelity, da Sterling da bankin Access, bisa zargin su da karya dokokin cinikayyar bankunan kasar, da hadin gwiwar tsohuwar ministar albarkatun mai ta kasar Diezani Alison-Madueke. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China