in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin ya amsa tambayoyi game da ziyarar da shugaban Amurka zai kai Japan
2016-05-12 10:44:43 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana cewa, a kusan karshen yakin duniya na biyu, kasar Amurka ta jefa makaman nukiliya guda biyu a biranen Hiroshima da Nagasaki, wadanda suka dakile yunkurin sojojin kasar Japan, amma kuma suka haddasa mutuwa da raunatar da dama daga fararen hula a kasar ta Japan, wadanda ya kamata a tausaya musu.

Mr. Lu Kang, wanda ya bayyana hakan a jiya Laraba yayin da yake amsa tambayoyi game da ziyarar da shugaban kasar Amurka Barack Obama zai kai birnin Hiroshima na kasar ta Japan, ya kara da cewa yakin duniya na biyu ya bayyanawa al'ummar duniya darasi daga tarihi, game da muhimmancin hana sake aukuwar irin wadannan yake-yake, da tabbatar da zaman lafiya a duniya bisa dokokin da aka kafa bayan yakin.

Ya ce Sin tana fatan Japan za ta shirya ziyarar shugabannin sauran kasashen duniya a Hiroshima ne, bisa tushen kauracewa ci gaba da bin ra'ayin nuna karfin soja, wadda ta taba kawo babbar illa ga jama'ar kasar ta Japan, da ma jama'ar nahiyar Asiya da na duniya gaba daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China