in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta soki ziyarar da jami'an Japan suka kai wurin Ibadan Yasukuni
2015-10-19 19:18:15 cri
Kasar Sin ta soki addu'ar da firaministan Japan Shinzo Abe da kuma ziyarar da ministocinsa biyu suka kai wurin Ibadan nan na Yasukuni da ake takaddama a kai a lokacin bikin bazara na kwanaki na hudu da aka saba gudanarwa kowa ce shekara a kasar.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying wadda ta bayyana hakan a yau, ta ce, kasar Sin tana bukatar Japan ta waiwayi tarihi kana ta kalli irin ta'asar da ta aikata a baya, sannan ta kaucewa duk wani mataki na amfani da karfi domin ta samu amincewa daga makwabtanta da kuma sauran al'ummomin kasa da kasa.

A jiya ne ministan shari'a na kasar Japan Mitsuhide Iwaki da takwaransa na harkokin cikin gida da sadarwa Sanae Takaichi suka ziyarci wurin Ibadar da ake kallo a matsayin wurin da aka karrama mutanen da suka tafka danyen aiki a duniya, yayin da shi kuma Abe ya aiki da sakon addu'a a gabanin ziyarar tasu.

Kasashen Sin da Koriya ta Kudu sun yi allah-wadai da ziyarar da jami'an kasar ta Japan suka kai wurin Ibadar na Yasukuni.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China