in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A karon farko jiragen ruwan yakin kasar Sin sun kai ziyara kasar Sudan
2015-08-26 09:36:44 cri
A jiya da safe ne, tawagar jiragen ruwan yaki na kasar Sin mai lamba 152 wadda take gudanar da ayyukan kai ziyara a kasashen duniya ta isa mashigin tekun Sudan, inda ta fara ziyarar kwanaki 5 a kasar Sudan. Wannan ne karo na farko da jiragen ruwan yaki na kasar Sin suka ziyarci kasar ta Sudan.

A yayin ziyarar, ana sa ran jama'a za su kalli jiragen ruwan yakin, inda za a shirya liyafa a kan jirgaren ruwan, da ziyartar gidan marayu, shirya gasar wasan kwallon kafa tare da sojojin ruwa na Sudan da dai sauransu.

Mashigin tekun Sudan yana arewa maso gabashin kasar ne, wanda shi ne hanyar cinikayyar kasashen waje daya tilo ga kasar ta Sudan, kuma ana kiran mashigin da suna "mashigar kasar Sudan". (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China